Shugaban Bola Tinubu ya nada Abba Aliyu a matsayin shugaban hukumar samar da lantarki a karkara


Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada Abba Abubakar Aliyu a matsayin babban Manajan Darakta na Hukumar bunkasa wutar lantarki a yankunan karkara (REA).
 
Wata sanarwa da Bayo Onanuga mai taimaka wa shugaban kan yada labarai ya fitar, ta ce nadin ya fara aiki daga 23 ga watan Junairu 2025.
 
Abba Abubakar Aliyu ya rike da mukamin mukaddashin manajan daraktan hukumar tun watan Maris na 2024 har zuwa lokacin da aka nada shi.
 
A baya, ya rike mukamin shugaban sashin kula da ayyuka na shirin samar da wutar lantarki ta Najeriya

Shugaba Tinubu ya yi ammanar cewa, Abba Aliyu zai yi amfani da dimbin ƙwarewar da yake da ita  don kara kawo  cigaba a hukumar.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp