Shugaba Tinubu zai je Hadaddiyar Daular Larabawa domin halartar wani taron


Shugaban Nijeriya Bola Ahmad Tinubu zai bar birnin tarayya Abuja a ranar Assabar 11 ga watan Janairu, domin halartar taron tattaunawa kan matsalolin da ke addabar duniya na shekara ta 2025 da zai gudana a birnin Abu Dhabi na Hadaddiyar Daular Larabawa.

Wannan na kunshe ne a cikin sanarwar da mai magana da yawun fadar shugaban kasa Bayo Onanuga, ya fitar a yau jumu'a.

A cewar sanarwar, Shugaban Hadaddiyar Daular Larabawa Sheikh Mohamed bin Zayed Al Nahyan, shine ya gayyaci Shugaba Tinubu domin ya halarci taron da zai gudana daga ranar 12 zuwa 18.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp