Nijeriya za ta karbi bakuncin taron samar da rigakafin cutar Lassa Fever na kasashen yammacin Afrika


Gwamnatin Nijeriya za ta karbi bakuncin taron samar da rigakafin cutar Lassa Fever na kasashen yammacin Afrika da zai gudana a ranar Laraba 15 ga watan Janairu.

Ministan Lafiya Farfesa Muhammad Pate ne ya bayyana hakan a firarsa da gidan talabijin na Channels.

Cutar zazzabin Lassa dai annoba ce da ta hallaka mutane 191 kuma take yin barazana ga jihohin Nijeriya dama wasu kasashen Afrika.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp