Nijeriya ta karbi kadarori da suka fi sama da dala miliyan hamsin da biyu da aka kwato hannun tsohuwar ministar mai Diezani


Gwamnatin Nijeriya ta ce ta karbi miliyan 52.88 daga kasar Amurka da aka kwato wadanda aka alakanta da tsohuwar ministar mai Diezani Alison-Madueke.

Babban lauya na kasa kuma ministan shar'ia Lateef Fagbemi ne ya bayyana hakan a lokacin da yake sanya hannu kan yarjejeniyar mika kadarorin tsakanin Nijeriya da Amurka a Abuja.

Fagbemi ya ce dala miliyan hamsin daga cikin kudaden za a yi amfani da su a karkashin shirin bankin duniya na samar da lantarki a yankunan karkara, yayinda sauran dala miliyan biya za a sanya su a inganta bangaren shari'a domin ya ki da cin hanci da rashawa.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp