Nijeriya na da isassun kuɗin da Shugaba Tinubu zai yi tafiye-tafiye kasashen duniya - Ministan harkokin waje

Ministan Harkokin Wajen Nijeriya Yusuf Tuggar, ya ce Nijeriya na da isassun kuɗin da za ta iya daukar nauyin tafiye-tafiyen Shugaba Bola Tinubu zuwa kasashen ketare.

Ministan ya bayyana hakan ne a cikin shirin siyasa da gidan talabijin na Channels ke gabatarwa.

Wasu ‘yan Nijeriya dai na yin guna-guni kan yadda shugaban kasar ke yin balaguro daga kasa zuwa kasa, ba tare da kasar ta samu wani ci gaba ba.

Sai dai Ministan ya yi watsi da wannan, inda yace ziyarar shugaban ta jawo wa Nijeriya masu zuba hannun jari da suka saka dala biliyan 2 bayan ziyarar da ya kai a ƙasar Brazil.

Tun bayan hawa karagar mulki a shekarar 2023, rahotanni sun ce Shugaba Tinubu ya ziyarci kasashe kusan 19 a tafiye-tafiye 32 kasashen ketare.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp