Nan gaba kaɗan za a ƙara kudin kira, data da sms - Gwamnatin Nijeriya


Gwamnatin Nijeriya ta ce dole ne a kara kudin amfani da layin sadarwa na kasar domin bunkasa bangaren da kuma hannayen jari da aka zuba.

Sai dai gwamnatin ta ce karin da za a yi ba zai kai kashi 100 ba kamar yadda kamfunna ke bukata.

Ministan sadarwa da tattalin arziki na zamani Dr Bosun Tijani ne, ya bayyana hakan a Abuja, jim kadan bayan wata ganawa da masu ruwa da tsaki kan harkokin sadarwa.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp