Mutune 7 sun riga mu gidan gaskiya, yayin da sama da 80 suka jikkata sanadiyar fashewar motar man fetur da ta fadi a Suleja jihar Neja


Akalla mutane 7 ne ake hasashen sun mutu yayinda wasu 80 suka ji munanan raunuka sanadiyar motar dakon mai ta fashe a kan hanyar Maje-Dikko dake karamar hukumar Suleja ta jihar Niger.

Shaidun gani da ido sun shaida wa jaridar Dailynigerian cewa lamarin ya faru ne da sanyin safiyar Asabar lokacin da ake juye mai daga motar zuwa wata.

Jami'an tsaro da na kashe gobara sun hallara a wurin domin kashe gobarar da ta tashi.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp