Muna neman kari a kasafin kudi don samar da ayyukan yi - Ministan kwadago da samar da ayyukan yi Muhammad Dingyadi

 

Ministan kwadago Muhammad Dingyadi

Ministan kwadago da samar da ayyukan yi, Muhammad Dingyadi, ya ce ma’aikatar na bukatar karin kudade cikin kasafin kudin 2025, domin bunkasa ayyukan ta.

Ya ce za a yi amfani da kudaden musamman wajen gyarawa, sake ginawa da kuma samar da kayan aiki ga cibiyoyin bunkasa sana’o’i da ke karkashin ma’aikatar da hukumomi a fadin kasar, da nufin samar da ayyukan yi ga al'umma.

Dingyadi ya bayyana haka ne a lokacin da yake kare kasafin kudin 2025, a gaban kwamitin majalisun dokoki da na dattawa. Ya ce jimillar kasafin naira biliyan 46 da aka ware wa ma’aikatar a wannan shekarar ba zai wadatar ba wajen cimma manufofin da ake so a cimma.

Dangyadi ya jaddada cewa samar da ayyukan yi ta hanyar bunkasa fasahar zamani na da matukar muhimmanci wajen cimma wani bangare na manufofin gwamnatin shugaba Tinubu.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp