Mulki ba zai sanya na sauya daga yadda aka sanni ba - Gwamnan Rivers Sim Fubara

Gwamnan jihar Rivers Siminalayi Fubara, ya ce ba zai bari giyar mulki ta sauya shi ba daga yadda yake.

Gwamnan ya bai wa al'umma tabbacin zai tsaya kan alkawuran  da ya yi wa al'ummar Rivers domin kawo ci gaba a jihar.

Gwamna Fubara ya yi wadan nan kalaman ne lokacin da dattawa da masu ruwa da tsaki na jihar suka kai masa ziyara domin taya shi murnar cika shekar 50 da haihuwa.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp