Kungiyar kwadago a Nijeriya NLC ta nace sai Shugaba Tinubu ya janye kudurin dokar haraji dake majalisa


Kungiyar kwadago NLC a Nijeriya ta dage akan cewa dole sai gwamnatin tarayya ta janye dokar garambawul ga haraji da ke gaban majalisar dokokin kasar.

A cikin sakonta na barka da sabuwar shekara, Shugaban kungiyar NLC Joe Ajaero ya ce wannan ya zama dole saboda inganta walwalar ma'aikatan Nijeriya.

Ya kuma jaddada muhimmancin aikin gwamnati a buɗe tare da janyo masu ruwa da tsaki da kuma yi wa 'yan kasa adalci a kowane lamari.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp