Kaso 9.6% na daliban makarantun firamaren jihar Kano ne kacal ke iya karatu, in ji wani rahoton Asusun UNICEF

 

Daliban Firamare

Shugaban ofishin UNICEF mai kula da shiyyar Kano, Rahama Mohammed, ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai na bikin ranar ilimi ta duniya ta shekarar 2025 a ranar Juma’a a Kano.

A cewarsa, jihar na fama da matsananciyar matsalar ilimi, inda yara kusan miliyan daya ba sa zuwa makaranta, bisa ga sabbin bayanai da suka fito.

Ya ce a halin yanzu kusan kashi 32 cikin 100 na yara ne ba sa iya shiga makarantun sakandire zuwa gaba da sakandire a jihar,don haka akwai bukatar ayi adinda ya dace wajen rage kason wa'yanda ba sa iya tsallake wannan mataki.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp