Kasar China ta yi alkawarin bayar da tallafin Yuan biliyan daya ga kasashen Afirka don tunkarar kalubalen tsaro

 

Ministan harkokin wajen kasar China Wang Yi/Shugaba Tinubu

Ministan harkokin wajen kasar China Wang Yi ne ya bayyana hakan ga manema labarai bayan tattaunawa da Shugaban Nijeriya Bola Tinubu a fadar sa dake Abuja.

Ya ce ta hanyar hadin kai da taimakon juna ga kasashen duniya ne za a iya kawo karshen kalubalen tsaro.

A cewar sa kasar China na son yin aiki tare da kasashen Afirka wajen aiwatar da shirin samar da tsaro da zaman lafiya a duniya,inda ya ce kasar tasu a shirye take ta bayar da gudun mawa wajen inganta tsaro a nahiyar Afirika.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp