Jiragen yaki sun yi luguden wuta tare da ajalin 'yan ta'adda da dama a jihar Neja


Wani farmaki da jiragen rundunar sojin saman Nijeriya suka kai a maboyar 'yan ta'adda ya yi sanadiyar mutuwar wadanda ake zargin 'yan bindiga da dama a dajin Alawa Forest cikin karamar hukumar Shiroro ta jihar Neja.

Rundunar ta ce an kai harin ne karkashin rundunar Operation Fansan Yamma dake yaki da 'yan bindiga a yankin Arewa ta Yamma da Arewa ta Tsakiyar Nijeriya.

Sanarwar da daraktan yada labarai na ofishin rundunar sojin saman Olusola Akinboyewa, tace an tarwatsa maboyar 'yan bindigar.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp