Jam'iyyar APC ta ja kunnen PDP kan zargin da ta yi na yunkurin hallaka Sanatan Kaduna ta Tsakiya



Jam'iyyar APC mai mulkin jihar Kaduna ta bukaci jam'iyyar PDP ta guje wa bata sunan APC ta hanyar yin zarge-zargen da basu da tabbas domin yada farfaganda.
 
APCn wadda ke martani kan zargin yunkurin hallaka Sanata Lawal Adamu Usman mai wakiltar Kaduna ta Tsakiya a majalisar dattawa, ta bayyana zargin a matsayin kage.

A cikin wani bayani da Sakataren APC Alhaji Yahaya Baba Pate ya fitar, ya shawarci PDP ta rika yin adawa mai ma'ana.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp