Hukumar sadarwa NCC ta umarci kamfanonin sadarwa su katse lambobin USSD na wasu bankuna

Hukumar sadarwa ta Najeriya NCC, ta umarci kamfanonin sadarwa da su katse lambobin aike sakonnin USSD na bankuna 9, a kasar sakamakon tarin bashin da ake bin su.

Hukumar ta tabbatar da hakan ne ta cikin sanarwar da jami'in yada labaran ma'aikatar ta NCC Rueben Muoka ya fitar a ranar Talata.

Hukumar ta ce ya yin da wasu bankunan suka biya bashin da ake bin su yanzu haka ana bin wasu kudaden da suka zarta sama da biliyan 200.

NCC ta ce ya zama wajibi Bankunan su biya basukan da ake binsu zuwa ranar 27 ga Janairun 2025; ko su rasa manhajar sakonnin ta USSD gaba daya.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp