Hukumar NAPTIP mai yaki da safarar mutane a Nijeriya ta ceto mata masu ciki 9 daga wani gida a Abuja


Hukumar yaki da safarar mutane a Nijeriya NAPTIP ta ce jami'anta sun ceto wasu mata masu ciki 9 da ke tsare a wani gida cikin birnin tarayya Abuja.

Wata sanarwa da jami'in yada labarai na NAPTIP, Vincent Adekoye ya fitar, ya ce gidan yin jariran yana unguwar Ushafa cikin Abuja.

A cewar Adekoye, kamen ya biyo bayan wani samame da jami'an NAPTIP suka kai bayan an kwarmata musu bayanin gidan.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp