Hukumar Hisbah a jihar Kano ta kama saurayi da budurwa bisa zargin daura aure ba tare da izinin iyayensu ba a wani wurin cin abinci

 

Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa

Mataimakin babban kwamandan hukumar, Dakta Mujahideen Abubakar, ya tabbatar da kamen ga jaridar PUNCH a ranar Alhamis, inda ya bayyana cewa jami’an Hisbah sun kai farmaki gidan abincin ne a daren ranar Larabar, biyo bayan samun bayanan sirri.

Ya ce abin takaicin ma shine saurayin tare da abokan sa ne suka gudanar da daurin auren a gidan abincin ba tare da amincewar iyayen su ba.

Ya yi gargadin cewa hukumar ba za ta zuba ido tana kallon ana yin wasu abubuwan da basu dace ba, da za su keta shari’a a fadin  jihar.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp