Hakkin 'yan Nijeriya ne a samar masu da wadataccen abinci ba alfarma ba-Tajudden Abbas



 Hakkin 'yan Nijeriya ne a samar masu da wadataccen abinci ba alfarma ba-Tajudden Abbas

Shugaban Majalisar Wakilai, Abbas Tajudeen, ya ce samar da abinci wani babban hakki ne na ‘yan kasa ba gata ba.

Abbas ya bayyana haka ne a Abuja a lokacin da yake gabatar da jawabinsa a matsayin babban bako a taron tattaunawa na shekara-shekara 

Ya kuma tabbatar wa ‘yan Nijeriya kudurin Majalisar Dokoki ta kasa na kafa dokar da za ta bunkasa  noma tare da tabbatar da wadatar abinci a fadin kasar.

Shugaban majalisar  ya samu wakilcin shugaban kwamitin kula da wadatar abinci na majalisar, Dike John Okafor.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp