Gyaran dokar haraji na daga cikin manya-manyan batu da majalisar Nijeriya za ta yi muhawara kansu a yau bayan dawowa daga hutu

 

Yayin da majalisar dokokin Nijeriya ta koma aiki a yau, 'yan majalisar daga yankin arewa sun kammala shirye-shiryen rufe majalisa idan har ba a janye kudirin gyaran haraji da ke gaban majalisar ba.

Sun nanata kiran da suka yi na a janye kudirin saboda rashin tuntubar masu ruwa da tsaki game  abubuwan da kudurorin suka kunsa, a cewar jaridar Dailytrust.

Don magance wadannan matsalolin, majalisar dattawa ta kafa wani kwamiti karkashin jagorancin shugaban marasa rinjaye Sanata Abba Moro don ganawa da babban lauyan tarayya don magance korafe-korafen da suka shafi kudirin.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp