Gwamnonin Nijeriya za su ci gaba da bai wa shugaban kasar goyon baya wajen magance tsaro da ci gaban tattalin arziki-Gwamnan Kwara

 

Abdulrahman Abdulrazaq

Shugaban kungiyar gwamnonin Nijeriya gwamnan jihar Kwara, Abdulrahman Abdulrazaq, ya yaba wa manufofin tattalin arziki na shugaba Bola Tinubu dake kara habbaka jihohin kasar.

Abdulrazaq ya bayyana hakan ne a ranar Laraba, yayin bikin sabuwar shekara da mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima da mambobin kungiyar gwamnonin Nijeriya suka kai wa shugaban kasar a gidansa da ke da ke Legas.

Gwamnan ya kuma bayyana nasarorin da aka samu a harkar noma a karkashin gwamnatin Tinubu, inda ya bayar da misali da yadda aka samu amfanin noma mai yawa a jihar Jigawa.

Abdulrazaq ya baiwa shugaban tabbacin ci gaba da bayar da goyon baya wajen magance kalubalen tsaro da ci gaban tattalin arziki.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp