Gwamnatin Tinubu ta himmatu wajen kyautata rayuwar ‘yan Nijeriya – Sakataren gwamnatin tarayya Geoge Akume

 

Geoge Akume

Sakataren gwamnatin tarayya, George Akume, ya bayyana aniyar shugaba Bola Tinubu na ciyar da 'yan kasar ribar dimukradiyya ta hanyar kyautata rayuwar su.


Akume ya bayyana hakan ne a ranar Larabar a wajen taron da aka gudanar don karrama babban daraktan Kula da Gidaje ta Tarayya, Mathias Byuan, a Jihar Binuwai.


Akume, yayin da yake kaddamar da ayyukan tituna da gwamnatin tarayya ta fara aiwatarwa a fadin jihar, titin Makurdi/Mile, ya umurci matasa da su rika neman a ba su hakkinsu na tafiyar da harkokin siyasa ba kawai su zauna su yi shiru ba,su zamo masu jajircewa a koda yaushe.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp