Dazuka ya kamata ku karbe don magance ayyukan ta'addanci, shawarar Ganduje ga sojojin Nijeriya

 

Abdullahi Umar Ganduje

Shugaban jam’iyyar APC, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya bayyana bukatar sojoji su kakkabe dazuka domin kawo karshen ‘yan ta'adda a Nijeriya.

Ganduje ya bayyana haka ne a lokacin da ya kai ziyarar jajantawa ga gawamnatin jihar Neja, kan faduwar tankar mai da ta yi sanadiyyar mutuwar mutane da dama a jihar.

A wata sanarwa da babban sakataren yada labaran sa, Edwin Olofu, ya fitar a ranar Alhamis a Abuja, shugaban jam’iyyar APC ya jaddada bukatar daukar matakan da suka dace da kuma daukar matakai masu tsauri, musamman ga masu aikata laifuka da suka buya a cikin dazuzzuka, don kawo karshen su a fadin kasar.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp