Dandalin dattawan yankin arewacin Nijeriya sun sake nuna damuwa akan kudurin dokar garambawul ga haraji da gwamnatin tarayya ta gabata, inda suka bukaci a dakatar da dokar tare da tattaunawa da masu ruwa da tsaki.
Dattawan sun soki matakin gwamnati na kin janyo kwararru da masu ruwa da tsaki kafin a rubuta dokar.
A cikin wata sanarwa da suka fitar a jiya Assabar, dauke da sa hannun shugaban dandalin Al-Amin Daggash, dattawan sun nuna damuwa dokar, wadda suka ce za ta iya mayar da yankin arewa baya da kasar baki daya.
Category
Labarai