Bani da tabbacin kididdigar yawan marasa aikin yi a Nijeriya - Ministan kwadago Maigari Dingyadi

Ministan Kwadago Muhammad Dingyadi

Ministan kwadago da samar da ayyukan yi, a Nijeriya Muhammadu Dingyadi, ya ce bai da tabbacin kididdigar marasa ayyukan yi a kasar, amma ya sha alwashin ma’aikatarsa ​​za tai kokari wajen magance rashin aikin yi.

Dingyadi ya bayyana haka ne a ranar Litinin yayin da ya bayyana a gaban kwamitin majalisar dattawa mai kula da ayyukan yi da kwadago karkashin jagorancin Sanata Diket Plang.

Ya ce bai kai wata uku a ofishin sa ba, zuwa yanzu bashi da wata kididdiga ta marasa ayyukan yi,amma ma'aikatar na kokari wajen ganin an samu gurabe da samar da damarmaki a fadin kasar.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp