'Yan bindiga sun yi ajalin ‘yan kasuwa tare da raunata mutum 11 a Fika a jihar Yobe

 

Gwamnan jihar Yobe Mai Mala Buni


Yan bindigar ana  zargin sun kai farmaki kasuwar da ke ci duk sati a Ngalda karamar hukumar Fika da misalin karfe 6 na yammacin ranar Litinin da suka yi  harbe harbe tare da  fasa shaguna a kasuwar.

Wani dan karamar hukumar Fika Dauda Yakubu Damazai, ya shaida wa Daily Trust cewa wasu ‘yan kasuwa guda bakwai a babbar kasuwar shanun sun rasa rayukansu a wannan mummunan hari.

Ya ce da yammacin ranar wasu da ba a san ko su waye ba sun kai hari a kasuwar shanu da babbar kasuwar inda suka  kashe mutane bakwai tare da jikkata mutane 11, kuma tuni aka  garzaya da su babban asibitin Fika domin duba lafiyar su.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp