Ana ci gaba da musayar kalamai tsakanin Peter Obi da shugaban jam'iyyar APC Abdullahi Umar Ganduje

 

Ganduje/Peter Obi

Dan takarar shugaban kasa na Jam'iyyar Labour Party a zaben 2023 da ya wuce Peter Obi ya ce kalaman da mai magana da yawun jam'iyyar APC Felix Morka ya yi a baya bayan nan ya saka shi shida iyalin sa cikin hadari.


Sai dai a bagare daya shugaban shugaban jam'iyyar APC Abdullahi Umar Ganduje, ya bayyana kalaman na Obi, a matsayin neman bata suna.


A cikin wata sanarwa da Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya sanya wa hannu, ya bayyana batun a matsayin abin takaici da bisa ikirarin da Peter Obi ya yi cewa ana yimasa barazana shi da iyalinsa.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp