An tsige kakakin majalisar dokokin jihar Lagos Mudashiru Obasa


Mambobin majalisar dokokin jihar Lagos sun tsige shugaban majalisar Mudashiru Obasa.

Hakama an nada mataimakiyarsa Mojisola Meranda, a matsayin wadda za ta maye gurbinsa, mace ta farko da ta riki mukamin a jihar Lagos.

Tsige Mudashiru Obasa na zuwa ne kasa da wata daya da aka zarginsa da kashe naira biliyan 17 wajen gyara kofar shiga majalisar.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp