Al-Hilal ba za ta yi wa Neymar Jnr rijista ba

Kungiyar kwallon kafa ta Al Hilal dake kasar Saudi Arabia, ba zata yi wa gwarzon dan wasan kasar Brazil Neymar Junior rijistar buga zagaye na biyu na gasar kakar wasannin firimiyar kasar ba ta 2025.
Hakan ya biyo bayan nazarin lafiyar dan wasan da tawagar ta yi na irin gudunmowar da zai bawa kungiyar.
A baya Neymar ya samu zunzurutun kudi Euro Miliyan 101 a shekarar 2024, a wasanni biyu kacal da ya shafe mintuna 42 a cikin filin wasa.
Ya shafe tsawon watanni 6, ya na fama da jinyar rauni abinda ya sa a yanzu haka Al Hilal ke dari -darin tsawaita kwantiragin sa.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp