AFCON 2025: CAF ta sanya Najeriya a 'rukunin C' mai kasashen Tunisiya, Uganda da Tanzania

 

Shugaban Nijeriya sanye da rigar Super Eagles

Tawagar kwallon kafa ta Najeriya Super Eagles ta samu kanta a rukunin C bayan raba jadawali na rukuni a gasar Kofin nahiyar Afrika,  AFCON ta 2025 da za a yi a kasar Morocco.


Daga cikin abokanan karawar ta Super Eagles a rukunin akwai kasar Tunisia sai Uganda da Tanzania.


Kasashen da ke rukunin A sun kunshi Morocco mai masaukin baki sai Mali da Zambia kana Tsibirin Comoros.

Daga rukunin B kasashen Masar wato Egypt da Afirka ta Kudu sai Angola da Zimbabwe ne za su kece raini.

Rukunin D akwai kasar Senegal da Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango  sai Jamhuriyar Benin da Botswana.

Rukunin E na dauke da kasashen Algeria da Burkina Faso sai Equatorial Guinea da Sudan. Sai rukunin karshe na F mai kasashen Cote d'Ivoire kana Cameroun da Gabon tare da Mozambique.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp