'Yan bindiga sun kai wa ayarin motocin mahaifiyar gwamnan Taraba hari

 

Wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne sun kai hari kan mahaifiyar gwamnan jihar Taraba, Jumai Kefas da kuma ‘yar uwar sa, Atsi.

Lamarin ya faru ne a jiya a kan hanyar Wukari zuwa Kente a karamar hukumar Wukari

Shugaban karamar hukumar Wukari Dauda Samaila Agbu ya tabbatar da faruwar lamari inda ya bayyana shi a matsayin "mai matukar tayar da hankali" 

Kanwar gwamna mai suna Atsi Kefas ta samu harbin bindiga, inda da farko aka fara yi mata jinya a asibitin koyarwa na gwamnatin tarayya da ke Wukari kafin a dauke ta zuwa Abuja domin ci gaba da kula da lafiyarta.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp