Tinubu zai gabatar da kasafin kudin shekarar 2025 a gaban Majalisun dokokin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu 

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu zai gabatar da kudirin kasafin kudin shekarar 2025 na naira tiriliyan 47 da Biliyan 900 ga Majalisun dokokin kasar. 

Shugaban majalisar dattawa Godswill Akpabio, ne ya bayyana hakan a zaman majalisar na ranar Alhamis. 

A 'yan makwannin da suka gabata ne Tinubu ya gabatarwa majalisun biyu, daftarin kasafin kudin na matsakaicin zango da ya kai Naira tiriliyan 26 da biliyan 100.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp