Tinubu ya nemi goyon bayan kafafen yada labarai kan kudirin dokar haraji



Tinubu ya nemi goyon bayan kafafen yada labarai kan kudirin dokar haraji

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya bukaci goyon bayan kafafen yada labarai kan kudirin sake fasalin harajin kasar, yana mai bayyana hakan a matsayin wani muhimmin mataki na gina kasa da kuma wadata ga yan Najeriya.

Shugaban wanda ya samu wakilcin Ministan Yada labarai na kasa, Mohammed Idris, ya yi wannan bayani ne a Lagos 

Ya kara da cewa duk da banbancin ra'ayi a tsakanin al'umma game da dokar haraji, amma akwai bukatar yin garambawul ga tsarin tafiyar da haraji a halin yanzu.

Ya jaddada kwarin gwiwar cewa, tattaunawar da ake yi kan sauye-sauyen haraji, za a samu mafita.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp