Tinubu ya janye nadin da ya yi wa Ambassador Haruna Ginsu da sauran wasu mukamai


 


A karshen watan Satumba ne shugaban na Nijeriya ya aike da sunan Ambassador Haruna Ginsu a matsayin shugaban hukumar gudanarwa ta sabuwar hukumar ta Northwest Development Commission tare da nada Senata Tijani Yahaya Kaura da Hon. Abdulkadir S. Usman a matsayin mambobi. Sai dai sanarwar da fadar shugaban kasa ta fitar ta baya-bayan nan ta ce Shugaba Tinubu ya musanya sunayensu da Ja'afar Abubakar Sadeeq da Yahaya Aminu Abdulhadi, yayin da ya ayyana Lawal Samaila Yakawada a matsayin shugaba. Sai dai sanarwar ta ce har yanzu Farfesa Abdullahi Shehu Ma'aji shi ne manajan daraktan hukumar

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp