Shugaban Nijeriya Bola Ahmad Tinubu ya mika sakon ta'aziyya tare da karantawa al'ummar kasar Indiya, kan rasuwar tsohon firaministan kasar Dr Manmohan Singh.
Dr Singh, wanda ya yi jagoranci tsakanin shekara ta 2004 zuwa 2014, ya rasu a jiya Alhamis yana da shekaru 92.
A cikin wani bayani da fadar shugaban Nijeriya ta fitar, ta hannun mai magana da yawun shugaban kasa Bayo Onanuga, Shugaba Tinubu ya bayyana Manmohan Singh a matsayin shugaba mai hangen nesa wanda ya yi tsayin daka wajen ganin alakar Nijeriya da Indiya ta yi karfafa.
Category
Labarai