Sakataren gwamnatin Jihar Bauchi ya yi murabus daga mukaminsa

Sakataren gwamnatin Jihar Bauchi ya yi murabus

Gwamnan jihar Bauchi Bala Muhammad Abdulkadir, ya amince da murabus din sakataren gwamnatin jihar Barista Ibrahim Kashim.

A wata sanarwa da mai taimakawa gwamnan na musamman kan harkokin yada labarai Mukhtar M Gidado, ya fitar a ranar Juma'a, ta nuna cewa murabus din ya fara aiki nan take. 

Sanarwar, ta kuma umarci shugaban ma'aikatan gidan gwamnatin jihar Dakta Aminu Hassan Gamawa, da ya rike mukamin a matsayin rikon kwarya ba tare da bata lokaci ba.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp