Nijeriya ta karbi tallafin rigakafin kyandar biri 11,200 daga Amurka


Nijeriya za ta karbi kashi na farko na tallafin rigakafin cutar kyandar biri daga kasar Amurka wanda kawance kasashe kan samar da rigakafi a duniya Gavi ya bayar.

Wani bayani da shugaban kawancen Dr Sania Nishtar ta fitar, ta ce maganin ya isa Abuja a wannan Jumu'a bayan wata yarjejeniya da Nijeriya ta sanyawa hannu a watan Nuwamba domin karbar tallafin rigakafin har 305,000 da za a yi amfani da su wajen ya ki da cutar kyandar biri a kasar.

A ranar 24 Satumba ne kasar Amurka ta bayyana kudurinta na samarda tallafin rigakafi milyan 1 domin tallafawa yakin da ake yi da cutar mpox da ta addabi wasu kasashen.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp