Matar hamɓararren shugaban kasar Siriya, Bashar Al'assad ta nemi takardar saki domin ta koma Burtaniya

 Matar hamɓararren shugaban kasar Siriya, Bashar Al'assad ta nemi takardar saki domin ta koma Burtaniya

Asma al-Assad, matar hambararren shugaban kasar Siriya Bashar al-Assad  ta shigar da karar neman saki daga mijinta tare da neman komawa kasarta Burtaniya. 

Jaridar Jerusalem Post ta ruwaito cewa Asma al-Assad ba ta jin dadin rayuwar gudun hijira da take yi tare da mijinta a birnin Moscow.

Ana dai zargin cewa Asma ta shigar da kara a gaban wata kotun kasar Rasha inda ta nemi izini ficewa daga kasar, yayin da mahukuntan kasar Rasha ke duba bukatarta, a cewar kafar yaɗa labarai ta NDTV.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp