Kungiyar ECOWAS ta matsa kaimi domin samar da kudin bai daya ga mambobin ta

 

Kungiyar ECOWAS ta matsa kaimi domin samar da kudin bai daya ga mambobin ta

Kungiyar ci gaban kasashen yammacin Afrika ECOWAS ko kuma CEDEAO, na ci gaba shirye-shirye kaddamar da kudin bai daya a yankin mai suna ECO, biyo bayan cimma matsayar da aka yi a yayin taron kasashen karo na 65.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwar karshen taron da shugabannin  kasashen suka gudanar karo na 66 a tarayyar Nijeriya Abuja.

A baya dai kungiyar ECOWAS dake da kasashe 15, ta shirya kaddamar da kudin ECK a shekarar 2020, amma cutar korona ta kawo tsaiko inda a halin yanzu aka sanya 2027 a matsayin ranar kaddamarwa.

Hukumar ta ce ta yi amfani da shawararin da babban kwamiti ya gabatar, na zabar kasashe da za a kaddamar da tsarin da kuma wadanda za su shigo daga baya.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp