Kuncin da talaka zai shiga ya sa Buhari ya ki cire tallafin man fetur - Adesina

Femi Adesina


Tsohon mai ba tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari shawara na musamman kan harkokin yada labarai da wayar da kan jama'a, Femi Adesina, ya bayyana ubangidan na shi a matsayin masoyin talaka. 

Adesina ya ce irin wannan la’akari ne ya sa ya yanke shawarar kin cire tallafin man fetur a matsayinsa na shugaban Najeriya.

Femi Adesina ya bayyana hakan ne a wani taron karramawa da aka yi wa Buhari wanda ya cika shekaru 82 a duniya.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp