Kirsimeti: Kungiyar kiristocin Nijeriya ta bukaci Tinubu ya rage farashin kayan abinci

Kungiyar kiristocin Nijeriya ta bukaci Tinubu ya rage farashin kayan abinci

Kungiyar kiristocin Nijeriya CAN ta bukaci gwamnatin tarayya da ta karfafa bangaren aikin gona da kuma rage farashin kayan abinci tare kuma da samar da daidaito a tsakanin yan kasa.

Shugaba Kungiyar Archbishop Daniel Okoh, ne ya mika wannan bukata a sakonsa na Kirsimeti ga mabiya addinin kirista, inda ya bukaci kiristoci da su rubanya riko da koyarwar Yesu domin wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a tsakanin al'umma musamman a irin wannan lokaci na tsanani.

Ya kuma nuna alhininsa game da yadda bikin na bana ya zo da wani irin yanayi na tausayi, musamman ganin yadda mutane suka rasa rayukansu a turmutsitsin karbar sadaka da ya gudana a Abuja da Ibadan da kuma Anambra.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp