John Dramani Mahama ya kayar da dan takarar jam'iyya mai mulkin Ghana a hukumance

John Dramani Mahama

Hukumar zaben kasar Ghana ta ayyana tsohon shugaban kasar kuma jagoran adawa John Dramani Mahama, a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasa na ranar Assabar.

Tuni mataimakin shugaban kasar kuma ɗan takarar jam'iyya mai mulki Mahamudu Bawumia, ya amince da shan kaye a zaben.

Hukumar zaben ta ce ta kirga kuri'un mazabun 'yan majalisa 267 daga cikin 276 na kasar, kuma Ya lashe kashi 56.55 na kuri'un.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp