Hukumar EFCC ta kama 'yan kasar waje 193, da wasu 599 bisa zargin zamba


Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta Nijeriya EFCC ta sanar da kama mutum 792 bisa zarge-zargen zamba a harkar kudaden kiripto da kuma soyayya.

Daraktan hulda da jama'a na rundunar Wilson Uwujaren, shi ne ya bayyana hakan ga manema labarai a Lagos.

Ya ce an kama wadanda ake zargin ne a yayin wani gagarumin samame da jami'an hukumar su ka kai maboyar masu aikata zamba, cikin wani gida mai hawa bakwai a unguwar Victoria Island da ke Lagos.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp