Hadin gwiwa tsakanin kasashen duniya zai tabbatar da dorewar kasuwar musayar hannayen - Dr Umar Kwairanga

Dr Kwairanga da takwaransa na India 

Kasuwar musayar hannayen jari ta Nijeriya NGX ta bukaci a yi hadin gwiwa tsakaninta da takwararta ta India, tana mai cewa hakan zai tabbatar da dorewar kasuwannin zuba jari a fannin tattalin arzikin duniya. 

Shugaban kasuwar ta NGX, Alhaji Umar Kwairanga ne ya bayyana haka a kasar India, yayin wata ziyarar hadin gwiwa da hukumar gudanarwar NGX ta kai kasar. 

A cewarsa, duniya na ci gaba da habaka cikin sauri don haka akwai bukatar hada gwiwa da nufin samarwa kasuwannin musayar hannayen jari kyakkyawar makoma.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp