Gwamnatin Tinubu ta himmatu wajen farfado da kwalejojin kimiyya da fasaha – Ministan ilimi


Ministan Ilimi Tunji Alausa, ya jaddada aniyar gwamnatin Najeriya na dawo da martabar ilimi a kwalejojin kimiyya da fasaha ta hanyar samar da nagartattun kayan aiki na zamani, da nufin samar da kwararrun dalibai da za su yi aiki tukuru wajen farfado da tattalin arzikin kasar.

Ministan wanda ya samu wakilcin Daraktan da ke kula da kwalejojin kimiyya da fasaha a ma'aikatar ilimi ta tarayya, Ejeh Usman, ya bayyana hakan ne ranar Talata yayin da yake kaddamar da dakunan karatu da na gwaje-gwaje da kayan aikinsu a kwalejin kimiyya da fasaha ta tarayya da ke Bali, a jihar Taraba. 

Ya ce gwamnati ta kashe makudan kuɗaɗe har Naira miliyan 390 domin gudanar da aikin, yana mai cewa shakka babu, aikin zai inganta koyo, koyarwa da bincike a kwalejin.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp