Gwamnatin Nijeriya za ta dauki ma'aikatan kwastam 3,927

 

Ministan kudi da tattalin arziki na Nijeriya, Wale Edun  ya ce gwamnatin tarayya ta amince da daukar ma’aikata 3,927 a hukumar kwastam da ke yaki da fasa kwauri.

A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar Abdullahi Maiwada ya fitar a ranar Lahadin da ta gabata, yace ministan ya bayyana haka ne a yayin taron hukumar karo na 61 a Abuja.

Ya kuma bayyana  muhimmancin da hukumar ke da shi wajen samar da kudin shiga ga gwamnatin tarayya musamman ga  kasafin kudin Najeriya na shekarar 2025.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp