Gwamnan Katsina ya nada sabon shugaban ma'aikatan gidan gwamnatin jihar

Gwamnan jihar Katsina ya amince da nadin Hon Abdulƙadir Mamman Nasir a matsayin sabon shugaban ma'aikatan fadar gwamnatin jihar.

Abdulƙadir Mamman Nasir ya maye gurbin Hon Jabiru Abdullahi Tsauri wanda Shugaba Tinubu ya nada mukami a Abuja.

Kafin nadin na Hon Abdulƙadir, shi ne shugaban hukumar kula da nomar rani ta jihar Katsina wato Katsina Irrigation Authority.

Bayanin hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun mai magana da yawun Gwamnan Malam Ibrahim Kaulah Mohammed da DCL Hausa ta samu kwafi a Katsina.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp