Gwamna Abba ya zargi 'yan adawa da rura wutar rikicin siyasa a Kano

Engineer Abba Kabir Yusuf 

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya zargi jam’iyyun adawa da rura wutar rikicin siyasa a Jihar.

Gwamnan ya yi wannan zargi ne lokacin da ya ke zantawa da manema labarai yayin taron majalisar zartarwar jihar a ranar Laraba, har ma ya bayyana aniyarsa ta daukar tsauraran matakan da suka dace don dakile sake barkewar ‘yan daba a Jihar. 

Wannan dai ya biyo bayan rikicin baya-bayan nan da ya barke tsakanin wasu da ake zargin ’yan bangar siyasa ne a Kano.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp