Filin da Wike ya kwace a Abuja ba na Buhari ba ne -Garba Shehu

Tsohon shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari 

Malam Garba Shehu, mai magana da yawun tsohon shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari, ya magantu game da labarin da ake yadawa cewa an kwace filin mai gidansa a Abuja.

A wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis, Garba Shehu, ya ce Buhari ba shi ne mai wannan filin da ake magana ba, an bayar da shi ga gidauniyar Muhammadu Buhari.

A baya-bayan nan ne wasu sunaye sama da 700 suka fita cewa ministan Abuja ya kwace takardun filayen ciki har da tsohon shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp