Daliban jami'ar Abuja sun yi watsi da sauya sunan jami'ar da Shugaba Tinubu ya yi


Daliban jami'ar Abuja sun yi watsi da sauya sunan jami'ar zuwa jami'ar Yakubu Gowon da gwamnatin tarayya ta yi tare da kira a gaggauta janye wannan mataki.

Daliban sun yi wannan kira ne a lokacin da su ka fito bakin kofar shiga jami'ar jiya Alhamis, rike da kwalaye da ke nuna cewa a bar jami'ar da tsohon sunanta, kamar yadda jaridar Dailytrust ta ruwaito.

Da yake jawabi a madadin kungiyar daliban Comrade Nkem Silas, ya nemi gwamnatin tarayya ta janye matakin saboda ɗaliban ba sa goyon bayan haka.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp