An yi kutse cikin shafin hukumar kididdiga ta Nijeriya

Tambarin NBS 

Hukumar kididdiga ta Nijeriya NBS ta sanar da cewa wasu batagari sun yi wa shafinta na intanet kutse. 

Hukumar ya bayyana hakan a wata sanarwa da aka wallafa a shafinta na X ranar Laraba, inda ta bukaci jama’a da su yi watsi da duk wani bayani ko rahoton da aka gani a shafin, har sai an shawo kan matsalar.

Hukumar ta baiwa jama'a tabbacin cewa tawagar kwararrunta na aiki tukuru domin kwato shafin daga hannun batagari.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp